Yanzu-yanzu: Kakakin majalisar jihar Yobe ya yi murabus, an zabi sabo

Yanzu-yanzu: Kakakin majalisar jihar Yobe ya yi murabus, an zabi sabo

Kakakin majalisar jihar Yobe, Adamu Dala-Dogo ya yi murabus daga mukaminsa.

Premium Times ta ruwaito cewa Mr Dala ya aike da wasikar murabus dinsa ga majalisar inda mataimakin majalisa, Ibrahim Kurmi ya karanto a zauren majalisar.

Ya yiwa takwarorinsa godiya bisa damar da suka bashi na rike mukamin kakakin majalisar.

Majalisar ta maye gurbin Mr Dala-Dogo da Zannah Machina bayan Ibrahim Kallalawa ya gabatar da kudirin zaben sabon kakakin majalisa kuma Ishaku Daya ya goyi bayan kudirin.

DUBA WANNAN: 2019: An ware 'yan takarar shugaban kasa biyu daga shiga muhawarar da za a fafata

Yanzu-yanzu: Kakakin majalisar jihar Yobe ya yi murabus
Yanzu-yanzu: Kakakin majalisar jihar Yobe ya yi murabus
Asali: Twitter

Mr Dala-Dogo da ke wakiltan mazabar Karasuwa a majalisar ya kwashe shekaru bakwai yana aiki a matsayin kakakin majalisar.

Jagoran majalisar, Usman Kabaruma mai wakiltar karamar hukumar Tarmuwa ya shaidawa manema labarai cewa Mr Dala-Dogo ya yi murabus ne domin ra'ayin kansa kamar yadda NAN ruwaito.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164