Takaitaccen tarihin sabon Shugaban Majalisar dokokin da aka zaba a Katsina

Takaitaccen tarihin sabon Shugaban Majalisar dokokin da aka zaba a Katsina

A makon da ya gabata ne Honarabul Tasi’u Musa Maigari ya zama sabon Kakakin Majalisar dokoki na Jihar Katsina. An zabi Musa Maigari ne bayan tsohon Kakakin Majalisar Jihar ya zama ‘Dan Majalisar Tarayya.

Takaitaccen tarihin sabon Shugaban Majalisar dokokin da aka zaba a Katsina
An nada Tasiu Maigari a matsayin Shugaban Majalisar Katsina
Asali: UGC

Mun kawo maku kadan daga cikin tarihin wannan Shugaban Majalisa da aka samu a Jihar Katsina kamar yadda mu ka tsakuro daga Jaridar Daily Trust. Ga kadan daga labarin rayuwar sa nan:

  1. Haihuwa

An haifi Musa Maigari a cikin Watan Afrilun 1966 a wani Kauye da ake kira Fuyumi a cikin Garin Zango a Yankin Daura. A nan Yankin Tasiu Maigari yayi karatun Firamare har zuwa 1978 inda ya wuce Garin Kaduna domin cigaba da ilmi.

KU KARANTA: Wani 'Dan majalisar tarayya na Katsina ya fice daga APC ya koma PDP

2.Karatun Boko

Rt. Hon. Maigari yayi Sakandare a Makarantar da ake kira Sardauna Memorial College (SMC) a Kaduna daga 1987 zuwa 1983, bayan nan kuma ya samu shaidar Difloma a Kaduna Polytechnic inda yayi karatu daga 1985 har zuwa shekarar 1988.

3.Aiki

Tasiu Maigari ya fara aiki ne a wani Kamfani a Fuyuni tun 1988 inda ya zama Darekta. Daga baya ya shiga siyasa har aka zabe sa ‘Dan Majalisar da ke wakiltar Zango a Jihar Katsina. Maigari shi ne Shugaban kwamitin lafiya a Majalisar.

4.Majalisa

Kwanaki ne Honarabul Ibrahim Dikko wanda yake wakiltar Matazu ne ya nemi a nada Tasi’u Musa Maigari ya maye gurbin Abubakar Yahaya Kusada inda Honarabul Sani Lawal da sauran ‘Yan Majalisa su ka amince da hakan ba tare da hamayya ba.

Idan ba ku manta ba, Abubakar Yahaya Kusada ya zama ‘Dan Majalisar Tarayya mai wakiltar Ingawa/Kusada/Kankia a zaben da aka yi kwanan nan. Kafin Kusanda, Aliyu Sabiu Maduru ya rike Majalisar kafin a tsige sa a farkon shekarar 2017.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa

Ko a http://twitter.com/legitnghausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta LEGIT NG Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Shafin NAIJ Hausa ya koma LEGIT

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng