Buhari ya nada Kabiru Bala a matsayin jakadan Najeriya a Afrika ta Kudu
Shugaba Muhammadu Buhari ya amince da nadin Kabiru Bala a matsayin jakadan Najeriya a kasar Africa ta Kudu da kuma kasashen Swaziland da Lesotho.
A wata sanarwa da ta fito daga bakin mai magana da yawun ministan harkokin kasashen waje, Sarah Sanda, Mr Bala ya karbi takardun kama aikinsa daga ministan harkokin kasa waje Geoffrey Onyeama.
Kafin yi masa wannan nadin, Mr Bala ya kasance shine mataimakin jakadan Najeriya a kasar Ingila.

Asali: Facebook
DUBA WANNAN: Gwamna Ganduje ya bawa hukumomin yaki da cin hanci gudunmawar miliyoyi
Ya fara aiki ne a ma'aikatar harkokin kasashen waje a shekarar 1999 kuma ya yi aiki a Brasilia, Sudan, Gambia, Nethelands da Thailand.
Ya kuma yi aiki a sassa daban-daban a ma'aikatan na harkokin kasashen waje da kuma fadan shugaban kasa da kuma ofishin babban mai tsaron shugaban kasa.
An bakaci ya tabbatar da cewa ya inganta dangata mai kyau tsakanin Najeriya ta Afrika ta Kudu.
An nada Mr Bala a matsayin jakadar Najeriya a Afrika ta kudu ne sakamakon murabus da Ahmed Ibeto ya yi bayan ya fice daga jam'iyya mai mulki ta All Progressives Congress, APC.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng