Dakarun soji sun samu nasara a kan gagararrun makiyayan Benuwe
Hedkwatar hukumar tsaro ta kasa ta bayyana cewar yanzu haka dukkan jama'ar da rikicin makiyaya ya shafa a jihar Benuwe sun koma gidajensu bayan ganin bayan 'yan ta'addar makiyaya da su ka addabi sassan jihar.
John Agim, darektan yada labaran hukumar tsaro, ne ya sanar da haka a yau, Asabar, tare da sanar da cewar atisayen soji ne ya kawo karshen aiyukan ta'addanci na makiyayan.
A cewar sa, jami'an soji sun rushe duk wani sansanin makiyaya da ke fadin jihar ta Benuwe.

Asali: Twitter
DUBA WANNAN: Buhari ya yi magana a kan kisan sojojin Najeriya 118
Agim ya kara da cewar nasarar da atisayen dakarun soji ya samu bai tsaya iya jihar Benuwe, ya shiga har jihohin Nasarawa da Taraba, da ke makwabtaka da jihar Benuwe.
A cewar sa, babu wani sansanin makiyaya da ya rage a jihar Benuwe kuma tuni jama'ar da su ka gudu sun koma garuruwansu na kakanni da iyaye.
Kazalika, Agim ya ce dakarun soji sun yi nasarar rage aiyukan ta'addanci na kungiyoyin 'yan bindiga daban-daban da ke jihar Benuwe.
Asali: Legit.ng