Hukumar 'yan sanda ta bayyana abinda ya haddasa rikicin Bauchi

Hukumar 'yan sanda ta bayyana abinda ya haddasa rikicin Bauchi

Hukumar 'yan sanda a jihar Bauchi ta bayyana cewar rikicin da ya barke ranar Lahadi a unguwar Yelwa da ke garin Bauchi, ba shi da alaka da addini ko kabilanci.

Hukumar ta ce sabani ne tsakanin wasu kungiyoyin matasa biyu da ta rikide zuwa rikici.

Wannan bayanai na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun DSP Kamal Datti Abubakar, kakakin rundunar, da hukumar ta fitar a yau, Laraba.

Sanarwar ta kara da cewar, hukumar 'yan sanda na wannan bayanai ne a matsayin raddi ga labaran da ke yawo a kafar sada zumunta da ke nuna cewar rikicin na da alaka da addini ko kabilanci.

Hukumar 'yan sanda ta bayyana abinda ya haddasa rikicin Bauchi
Hukumar 'yan sanda ta bayyana abinda ya haddasa rikicin Bauchi
Asali: Facebook

"Muna son sanar da jama'a cewar duk wani rahoto da ke nuna cewar an samu rikicin addini ko na kabilanci a jihar Bauchi ba gaskiya ba ne. Irin wadannan rahotanni sun samo asali ne daga jama'ar da basa son zaman lafiyar jama'a.

DUBA WANNAN: INEC ta bayyana ranar da za ai zaben gwamna da 'yan majalisar dokoki

"Binciken hukumar 'yan sanda ya tabbatar da cewar rikicin ya faru ne tsakanin wasu kungiyoyin matasa ta unguwar Yelwa da ke cikin garin Bauchi.

"Rigima ce tsakanin samari a kan budurwa a wurin wani biki, shine rikicin da ya shafi wasu ma su wucewa ta hanyar. Lamarin ya faru ne da misalin 10:00 na daren ranar Lahadi.

"Hukumar 'yan sanda ta samu rahoto a kan lokaci kuma nan da nan ta kwantar da rikicin," a cewar jawabin.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=ng.legit.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng