Kisan Janar Idris Alkali: Hoton mutane 19 da hukumar 'yan sanda ta yi bajakolinsu
- A yau, Lahadi, ne hukumar 'yan sanda reshen jihar Filato ta yi bajakolin wasu mutane 19 da ke da nasaba da kisan Janar Idris Alkali
- Kamfanin dillancin labarai na kasa (NAN) ta rawaito cewar an bayyana batan janar Alkali ne a ranar 3 ga watan Satumba bayan ya bar Abuja zuwa Bauchi
- A ranar 31 ga watan Oktoba ne aka gano gawar Janar Alkali a wata tsohuwar rijiya da yankin Gushwet a unguwar Shen a karamar hukumar Jos ta kudu
A yau, Lahadi, ne hukumar 'yan sanda reshen jihar Filato ta yi bajakolin wasu mutane 19 da ke da nasaba da kisan Janar Idris Alkali a garin Jos.
A yau ne kakakin rundunar 'yan sanda a jihar Filato, Terna Tyopev, ya yi bajakolin mutanen ga manema labarai a garin Jos.
Kamfanin dillancin labarai na kasa (NAN) ta rawaito cewar an bayyana batan janar Alkali ne a ranar 3 ga watan Satumba bayan ya bar Abuja zuwa Bauchi.

Asali: Twitter
A ranar 29 ga watan na Satumba ne aka samu motar janar Alkali a wani kududdufi mai zurfin gaske da ke yanki Dura Du a karamar hukumar Jos ta kudu.
A ranar 31 ga watan Oktoba ne aka gano gawar Janar Alkali a wata tsohuwar rijiya da yankin Gushwet a unguwar Shen a karamar hukumar Jos ta kudu. Hukumar soji ta binne gawar Marigayi Alkali a jiya, Asabar, 3 ga watan Nuwamba.
DUBA WANNAN: Tsige Oshiomhole: Gwamnonin APC sun fara neman hadin kan sanatocin da basu ci zabe ba
A cewar Tyopev, mutanen 19 sun hada da mutane 13 da hukumar soji ta kama kuma ta damka hannun jami'an 'yan sanda, yayin da ragowar 6 na daga cikin mutane 8 da hukumar ta sanda ta bayyana nemansu ruwa a jallo.
Kakakin ya kara da cewar, har yanzu rundunar 'yan sanda na cigaba da neman mutane biyu daga cikin wadanda ake zargi da kisan marigayi Alkali.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=ng.legit.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng