An kashe mutane 6 a wani sabon rikici a cikin Jihar Zamfara
Mun samu labari cewa an kashe mutane a wani hari da ‘Yan bindiga su ka kai Jihar Zamfara kwanan nan. An kai harin ne a wani Kauye da ake kira Gurbin Baure da ke cikin Karamar Hukumar Zurmi.
Wani babban Jami’in ‘Yan Sanda na Jihar Zamfara DSP Muhammad Shehu ya bayyanawa gidan rediyon BBC Hausa cewa wasu ‘Yan bindiga da ba a san iyakar su ba sun dura Kayen Baure cikin tsakar dare inda su kayi ta harbin Jama’a.
Jami’an tsaro sun tabattar da cewa akalla mutane 6 ne su ka bakunci lahira bayan harin da aka kai a cikin Karamar Hukumar ta Zurmi. Daga cikin wadanda aka kashe har da wani Jami’in ‘Dan Sanda inji Kakakin Jami’an tsaro na Jihar.
KU KARANTA: Sanata Shehu Sani ya bankado sirrin Gwamna El-Rufai
Abubakar Muhammad wanda shi ne Mataimakin Shugaban Hukumar ta Zurmi ya bayyanawa ‘Yan jarida cewa Jama’an Gari sun shiga cikin wani yanayi a halin yanzu yana kuma mai cewa wadanda aka kashe din sun wuce yadda ake tunani.
Ku na da labari cewa ba yau aka fara kai irin wannan munanan hare-hare ba domin kuwa an fi shekera guda ana kashe Bayin Allah a cikin wannan Gari na Zurmi. Wannan karo dai ‘Yan bingiga sun yi kone-kone bayan sun kashe Jama’a da dama.
Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa
Ko a http://twitter.com/legitnghausa
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta LEGIT NG Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Asali: Legit.ng