Tattakin Arbaeen: Artabu tsakanin mabiya Shi'a da sojoji ya yi sanadiyar mutuwar mutane 2
- Rahotanni sun bayyana cewar a kalla mutane biyu ne su ka rasa ransu bayan wani artabu tsakanin mabiya Shi'a da dakarun sojin Najeriya
- Jaridar Vanguard ta rawaito cewar an samu hatsaniya ne bayan sojojin da ke aiki a kan hanyar shiga Abuja sun hana mabiya Shi'ar wucewa
- A jiya, juma'a, ne kakakin kungiyar Shi'a ya sanar da 'yan jarida niyyar kungiyar na fara tattakin kwanaki uku daga ranar Asabar
Rahotanni sun bayyana cewar a kalla mutane biyu ne su ka rasa ransu bayan wani artabu tsakanin mabiya Shi'a da dakarun sojin Najeriya.
An samu hatsaniya tsakanin mabiya Shi'a da sojojin ne a unguwar Zuba da ke Abuja yayin da Shi'ar, daga Suleja, ke tattakin kwanaki uku (Arbaeen) zuwa Abuja.
Jaridar Vanguard ta rawaito cewar an samu hatsaniya ne bayan sojojin da ke aiki a kan hanyar shiga Abuja sun hana mabiya Shi'ar wucewa a daidai dutsen Zuma.

Asali: Facebook
Hakan ya fusata mabiyan na Shi'a da har ta kai sun fara jifan sojojin da duwatsu, su kuma su ka bude ma su wuta, lamarin da ya kai ga asarar rayuka biyu.
A jiya, juma'a, ne kakakin kungiyar Shi'a ya sanar da 'yan jarida niyyar kungiyar na fara tattakin kwanaki uku daga ranar Asabar.
DUBA WANNAN: 'Yan bindiga cikin kakin soji sun hallaka shanun makiyaya fiye da 150 a Taraba
Kungiyar ta bukaci mazauna garin Abuja da kar su tashi hankalin su, domin fiye da magoya bayan Zakzaky mutum miliyan daya za su gudanar da zanga-zanga a garin.
A cikin jawabin da Kungiyar mabiya Shi'a (IMN) ya fitar a daren jiya, ta tabbatar da mutuwar mutane 2.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta NAIJ.com Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng