Gasar karatun Al-Kur'ani: Dan asalin jihar Katsina ya bayar da mamaki a Saudiyya

Gasar karatun Al-Kur'ani: Dan asalin jihar Katsina ya bayar da mamaki a Saudiyya

- Wani dan asalin jihar Katsina, Abdulganiyu Aliyu ya zo na uku a fagen gasar karatun Al-Qurani mai girma na duniya da aka gudanar a Saudiyya

- Abdulganiyu Aliyu da Ameer Yunus daga jihar Bauchi ne suka wakilci Najeriya a wajen gasar da aka yi a birnin Madina

- Mutane 115 daga kasashen duniya 82 ne suka fafata a gasar karatun Al-Quranin da aka kammala ranar Laraba da ta gabata

Gasar karatun Al-Kur'ani: Dan asalin jihar Katsina ya bayar da mamaki a Saudiyya
Gasar karatun Al-Kur'ani: Dan asalin jihar Katsina ya bayar da mamaki a Saudiyya
Asali: Twitter

Wani dan asalin jihar Katsina da ya fito daga karamar hukumar Katsina, Abdulganiyu Aliyu ya yi nasarar zuwa na uku a gasar karatun Al-Qurani mai girma na kasa da kasa ta 2018 da akayi a kasar Saudiyya.

Abdulganiyu Aliyu ya fafata a gasar ne tare da sauran mallarta gasar guda 115 daga kasashe 82 na duniya.

DUBA WANNAN: Rikici: An shiga takun saka tsakanin Dankwambo da shugaban jam'iyyar PDP a Gombe

Legit.ng ta samo wannan labarin ne ta dalilin shafin Leadership wata ta zanta da mai bawa gwamnan jihar Katsina shawara na musamman kan ilimi mai zurfi, Mallam Bishir Usman Ruwan Godiya wadda ya yiwa Aliyu rakiya zuwa wajen gasar.

Abdulganiyu Aliyu da kuma Ameer Yunus daga jihar Bauchi ne suka wakilci Najeriya a wajen gasar da aka gudanar a birnin Madina da ke kasar Saudiyya.

Abdulganiyu Aliyu ya zo na uku a fannin hadar izihi 60 na gasar karatun Al-Qurani yayin da shi kuma Ameer Yunus ya zo na uku a bangaren hadar izihi 60 na Al-Qurani tare da tajawidi.

Kasar Saudiyya mai masaukin baki ita ce ta zo na farko sannan kasar Libiya da Najeriya suke biye da ita.

Wannan dai ba shine karo na farko ba da 'yan Najeriya ke nuna irin wannan bajinta a fagen gasar karatun Al-Qurani mai girma a fadin duniya ba.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta NAIJ.com Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164

Tags: