2019: Kwankwaso ba zai nemi kujerar Sanatan Kano ta tsakiya ba

2019: Kwankwaso ba zai nemi kujerar Sanatan Kano ta tsakiya ba

Mun samu labari cewa tsohon Gwamnan Jihar Kano Rabiu Musa Kwankwaso yayi watsi da tayin takarar kujeran da yake kai da aka yi masa ganin ya fadi zaben takarar Shugaban kasa a karkashin PDP.

2019: Kwankwaso ba zai nemi kujerar Sanatan Kano ta tsakiya ba
Aliyu Madakin Gini zai yi takaran Sanatan Kano ta tsakiya a PDP
Asali: UGC

Jam’iyyar adawa ta PDP da ‘Dan takarar da aka tsaida na Sanatan Kano ta tsakiya ta tuntubi tsohon Gwamnan ko zai yi kokarin zarcewa a kan kujerar sa. Sanata Rabiu Musa Kwankwaso dai ya nuna sha’awar bai da bukatar kujerar.

Sanata Rabiu Musa Kwankwaso yana cikin wadanda su ka rasa takarar kujerar Shugaban kasa a Jam’iyyar PDP a zaben da aka yi inda Atiku Abubakar yayi nasara. Yanzu dai ana ganin cewa ‘Dan siyasan ya tashi biyu-babu a PDP.

KU KARANTA: Abin da ya sa na kinkimo Ganduje ya zama Gwamna - Kwankwaso

Sauran ‘Yan takaran Shugaban kasa irin su Bukola Saraki da Rt. Hon. Aminu Tambuwal tuni su ka koma neman takaran kujerun da su ke rike da su. Sai dai Sanatan na Kano ta tsakiya ya nuna cewa bai sha’awar aikin Majalisa bayan 2019.

Yanzu haka dai ‘Dan Majalisar da ke wakiltar Dala a Majalisar Wakilai ta Tarayya Hon. Aliyu Madakin Gini shi ne zai nemi takaran kujerar Sanatan wanda Kwankwaso ya ke kai a 2019 inda zai kara da Malam Ibrahim Shekarau a APC.

Dazu kun ji cewa har yanzu rikicin Jam’iyyar PDP a Jihar Kano bai kare ba bayan da wani ‘Dan takaran Gwamna ya nemi Kotu ta dakatar da Surukin Rabiu Kwankwaso watau Abba Yusuf daga zaben 2019.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.naij.com

Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa

Ko a http://twitter.com/legitnghausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta LEGIT NG Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng