Tsohon shugaban kasar Sudan, Al-Dahab ya rasu a Saudiyya

Tsohon shugaban kasar Sudan, Al-Dahab ya rasu a Saudiyya

- Tsohon shugaban kasar mulkin soja na Sudan, Abdulrahman Al-Dahab ya rasu

- Al-Dahab ya rasu ne a babban birnin kasar Saudiya wato Riyadh

- Abdulrahman Al-Dahab ya rasu yana da shekaru 83 da duniya

Tsohon shugaban kasar Sudan, Al-Dahab ya rasu a Saudiyya
Tsohon shugaban kasar Sudan, Al-Dahab ya rasu a Saudiyya
Asali: Twitter

Tsohon shugaban kasar Sudan Abdulrahman Al-Dahab ya rasu a Riyadh, babban birnin kasar Saudiyya kamar yadda wani gidan talabijin na kasar, Al Arabiya ya ruwaito a jiya Alhamis.

DUBA WANNAN: Kungiyar Gwamnonin Najeriya ta bayyana matsayar ta kan batun karin albashi

Sai dai tashar talabijin din ba ta bayar da cikaken bayanin musababbin rasuwar na Al-Dahab ba. Al-Dahab shine shugaban kasa na biyar a tarihin Sudan kuma ya rasu ne yana da shekaru 83 a duniya.

Al-Dahab wanda tsohon soja ne ya mulki kasar daga ranar 6 ga watan Afrilun 185 zuwa 6 ga watan Mayun 1986 bayan ya yi juyin mulki a wancan lokacin inda ya hambarar da Nimeiry daga karagar mulki.

Tsohon shugaban kasar ya zaman Ciyaman din Gwamnatin mulkin soji a kasar har zuwa shekarar 1986 da aka gudanar da zabe sannan ya mika mulki ga Sadiq al-Mahdi kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) ta ruwaito.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164