Fusattatun 'yan gudun hijira sun farma tubabbun 'yan Boko Haram a Borno

Fusattatun 'yan gudun hijira sun farma tubabbun 'yan Boko Haram a Borno

- Tubabbun mayakan Boko Haram sun kusa haduwa da ajalinsu a sansanin 'yan gudun hijira da ke Maiduguri

- Hakan ya faru ne bayan wasu 'yan gudun hijira da ke sansanin sun gane fuskokinsu a matsayin wadanda suka kashe musu 'yan uwa a baya

- Rahotanni sun ce an kawo tubabbun 'yan Boko Haram din zuwa Maiduguri ne bayan sun kwashe watanni a wata sansanin da ke Gombe

Tubabbun mayakan kungiyar Boko Haram 51 da ke sansanin 'yan gudun hijira na Bakassi da ke Maiduguri suka tsira da rayyukansu da kyar bayan fusatattun 'yan gudun hijira da mayakan suka kashewa yan uwa sun harzaka domin daukan fansa kansu ranar Asabar da ta gabata.

Fusattatun 'yan gudun hijira sun farma tubabbun 'yan Boko Haram a Borno
Fusattatun 'yan gudun hijira sun farma tubabbun 'yan Boko Haram a Borno
Asali: Depositphotos

Daily Trust ta ruwaito cewar an fara kai tubabbun mayakan Boko Haram dun zuwa sansanin gudun hijira ne Bulumkutu ne da ke Maiduguri bayan sun kwashe wattani ana duba lafiyan kwakwalensu a sansanin yan gudun hijira d ake jihar Gombe karkashin shirin gwamnati na Operation Safe Corridor amma daga baya aka kai su sansanin gudun hijira da ke Gwoza.

DUBA WANNAN: Karshen duniya: An kama wasu matasa maza da mata 14 suna tika rawa zigidir a jihar Kebbi

Da isar su sansanin gudun hijrar ta Bakassi da ke Gwoza ne wasu da ke sansanin suka fara gane fuskokinsu a matsayin wadanda suka kashe musu iyaye, mata, mazaje da sauran 'yan uwa wadda hakan yasa suka yanke hukuncin daukan fansa kansu.

"Yan gudun hijiran sun farwa tubabbun 'yan Boko Haram din da suke zargin su ne suka kashe musu 'yan uwa da niyyar su dauki fansa a ranar Litinin da ta gabata," kamar yadda majiyar NAIJcom ta ruwaito.

Operation Lafiya Dole da sauran jami'an tsaro da ke yankin ba su yi tsokaci kan lamarin ba a lokacin rubuta wannan rahoton wani jami'in tsaro na sa kai 'Civilian JTF' ya bayyana cewar lamarin abin tsoro ne.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin Legit.ng Hausa zai koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164

Tags: