Da duminsa: Tsohon gwamnan PDP da ya koma APC sun gana da Buhari a Ingila, duba hotuna

Da duminsa: Tsohon gwamnan PDP da ya koma APC sun gana da Buhari a Ingila, duba hotuna

An yi wata ganawa tsakanin shugaba Muhammadu Buhari dsa shugaban marasa rinjaye na majalisar dattijai kuma tsohon gwamnan jihar Akwa Ibom, Godswill Akpabio, a kasar Ingila.

Idan baku manta ba, a jiya, Asabar, ne mai bawa shugaban kasa shawara a kan harkokin majalisar dattijai, Ita Enang, ya tabbatar da cewar Akpabio ya canja sheka daga PDP zuwa APC har ya sanar da cewar za a yi bikin karbar sa ranar 8 ga watan Agusta da muke ciki.

Tsohon gwamna Akpabio na daga kusoshin jam'iyyar PDP a yankin kudu maso kudu mai arzikin man fetur.

Akwai rahotannin cewar wasu gwamnoni PDP daga kudancin Najeriya zasu koma APC kafin zaben 2019.

Da duminsa: Tsohon gwamnan PDP da ya koma APC sun gana da Buhari a Ingila, duba hotuna
Buhari da Akpabio a Ingila

Da duminsa: Tsohon gwamnan PDP da ya koma APC sun gana da Buhari a Ingila, duba hotuna
Akpabio da Buhari

Enang ya sanar da hakan ne a jiya, Asabar, a shafinsa na Tuwita tare da bayyana cewar za a yi bikin karbarsa ranar 8 ga watan Agusta a jiharsa ta Akwa Ibom.

DUBA WANNAN: Mabiya Shi'a sun yi mauludin annabi Isa a Kaduna, duba hotuna

Ina mai tabbatar da tabbatarwa da jam’iyyar APC cewar, kamar yadda muka bayyana a baya, za a karbi Godswill Akpabio zuwa APC a ranar 8 ga watan Agusta a jihar Akwa Ibom”, kamar yadda sanarwar ta bayyana.

An dade ana jitar-jitar cewar tsohon gwamnan zai koma jam’iyyar APC musamman ganin yadda ya cigaba da kauracewa taron jam’iyyar PDP.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng