Albashin ma'aikata
Gwamnatin Anambra ta musanta wani rahoto da ke yawo wanda ya cire jihar daga jerin waɗanda suka yi ƙarin albashi, ta ce tun a watan Oktoba aka fara biya.
Kungiyar kwadago ta ƙasa watau NLC ta ce wa'adin da ta ba gwamnatocin jihohi kan fara biyan sabon mafi ƙarancin albashi yana nan daram, ta ce ba abin da ya sauya.
Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum ya amince da yi wa likitoci karin albashi a jihar. Gwamna Zulum ya amince a rika biyansu daidai da na tarayya.
Gwamnatin Bauchi ta sanar da lokacin fara biyan sabon mafi ƙarancin albashi a karshe watan Nuwamba. Bala Muhammad ya ce zai biya hakkokin ma'aikata a jihar.
Kungiyar 'yan kwadago a Zamfara ta yi barazanar tsuduma yajin aiki idan gwamnatin jiharba ta fara aiwatar da sabon mafi karancin albashi zuwa karshen Nuwamba ba.
Gwamnan jihar Ekiti, Dr. Biodun Oyebanji ya amince da N70,000 a matsayin sabon mafi ƙarancin albashin ma'aikatan gwamnati, ya ce har ƴan fansho za su ga canji.
Ministan Abuja, Nyesom Wike ya amince da biyan N70,000 ga ma'aikatan birnin Tarayya Abuja domin ragewa ma'aikatan halin tsadar rayuwa da ake ciki a Najeriya.
Gwamnan Benue ya yi karin mafi ƙarancin albashi zuwa N75,000 ga ma'aikata. Gwamnan ya ce ya kara albashi sama da yadda Tinubu ke biya a matakin tarayya.
Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa za a samu karin kaso 60 na kudaden albashin ma'aikatan tarayya a shekarar 2025 wand ake nufin cewa ma'aikatan za su kashe N6.5trn.
Albashin ma'aikata
Samu kari