Amurka
Babbar hedkwatar sojojin Najeriya ta jaddada cewa an samu nasara a farmakin da Amurka ta kai jihar Sakkwato, ta ce za a fitar da cikakkun bayanai nan gaba.
Kasashen Mali da Burkina Faso sun yi ramakon gayya kan matakin da Trump ya dauka na hana 'yan kasarsu shiga Amurka. Sun hana 'yan Amurka shiga kasashensu.
Shugaban Amurka, Donald Trump ya sanar da cewa ya kai wasu hare-hare wajen da ake lodin jiragen ruwa a kasar Venezuela. Ya ce sun yi barna sosai.
Tsohon dan takarar shugaban kasa, Gbenga Olawepo Hashim ya bayyana cewa harin Amurka ya nuna gazawar gwamnatin Shugaba Bola Tinubu da APC a Najeriya.
Shugaban Amurka, Donald Trump ya ce a shirye ya ke ya sake kai hare-hare Iran bayan ganawa da Benjamin Netanyahu. Ya bukaci kungiyar Hamas ta ajiye makami.
Kasar Amurka ta kawo hare-hare ta sama kan 'yan ta'adda a Najeriya. An kai hare-haren ne a Sokoto. Atiku Abubakar na daga cikin manyan da suka yi martani kan harin.
Dan majalisa a kasar Amurka, Riley Moore, ya yi tsokaci kan harin da Donald Trump ya ba da umarnin a kawo Najeriya. Ya ce an yi hakan ne don zaman lafiya.
Rahotanni sun nuna cewa mazauna kauyuka sun fara guduwa daga gidajensu saboda gudun Amurka ta sake jefo bama-bamai a yankunan jihar Borno a Arewa.
Wani masanin tsare-tsare da manufofin gwamnati a Najeriya, AbdulRasheed Hussain ya lissafi jihohi bakwai da ke bukatar dauki kak ayyukan ta'addanci.
Amurka
Samu kari