Amurka
A labarin nan, za a ji cewa babban jami'i a gwamnatin Amurka, Jonathan Burke zai shigo Najeriya domin ziyarar kwanaki biyu a kan batun ta'addanci.
Kasashen Greenland da Denmark sun yi watsi da tayin Donald Trump na tura jirgin asibitin ruwan teku domin kula da marasa lafiya a tsibirin Arctic.
Jami’an hukumar SS sun kashe matashi da makami a Mar-a-Lago na Trump. An harbe shi bayan ya shigo harabar yayin da Trump yana Washington a lokacin.
Kasashen Larabawa da Musulmi sun yi Allah-wadai da kalaman jakadan Amurka a Isra’ila, Mike Huckabee, kan fadada ikon Isra’ila, suna yin gargadi kan illolinsa.
Shugaban Amurka, Donald Trump ya zagi alkalan da suka hana shi kakabawa Najeriya da wasu kasashe haraji. Ya ce zai kawo sabon haraji na 10% kan kasashen duniya.
Ana ta ce-ce-ku-ce game da kudirin da wasu yan Majalisar Amurka suka gabatar wanda ya ambaci Rabiu Kwankwaso a cikin wadanda ake zargi da take hakkin kiristoci.
Kotun Koli ta soke kakaba harajin Donald Trump, ta ce bai da hurumi ba tare da amincewar Majalisa, yana jawo sabbin muhawara kan ikon shugaban kasa.
Alamu na nuni da cewa akwai yiwuwar Amurka ta kai hari kan Iran saboda shirinta na nukiya. Kasar Iran ta ba da tabbacin cewa za ta maida martani mai zafi.
Bincike ya bayyana dangantakar Jeffrey Epstein da Ehud Barak a harkar riba daga rikicin Boko Haram a Najeriya, tare da amfani da tashoshin jiragen ruwa da kan tsaro.
Amurka
Samu kari