Siyasar Najeriya
Gwamna Peter Mbah ya rantsar da sababbin kwamishinoni 6 tare da sauya wurin aikin wasu. Ya bukace su su fara aiki nan take domin kokarin cimma burikan gina Enugu.
Barau ya soki tantance Kaura saboda kasancewarsa tsohon sanata, amma Akpabio ya dage cewa bin ka’ida wajibi ne kafin amincewa da kowanne nadi da aka gabatar.
Tsohon ministan sufuri, Rotimi Amaechi, ya yi kalamai masu kaushi kan gwamnatin Bola Ahmed Tinubu. Ya sha alwashin kawo cikas ga tazarcensa a 2027.
Tsohon gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido ya yi kalaman zargi kan gwamnatin tarayya karkashin jagorancin mai girma Bola Tinubu. Ya ce ana son ganin bayan 'yan adawa.
Tsohon gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido, ya bayyana cewa a shirye yake ya shiga kowace irin tafiya ta siyasa idan har za ta kai ga ceto Najeriya a 2027.
Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio ya karaɓta takardun sauya sheƙar sanatoci huɗu daga PDP zuwa APC a zamansu na ranar Laraba, 23 ga watan Yuli, 2025.
Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya gana da 'yan majalisar jam'iyyar NNPP a Abuja kwanaki kadan bayan haduwa da shugaba Bola Tinubu a fadar shugaban kasa.
Yusuf Datti Baba-Ahmed ya ce ba shi da burin tsayawa takarar shugaban kasa a 2027 sai dai idan wasu mutum biyu da yake girmamawa ba su tsaya takarar ba.
Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Alhaji Atiku Abubakar ya ce barazanar da aka yi wa tsohon gwamnan Anambra, Peter Obi barazana ce ga duka ƴan Najeriya.
Siyasar Najeriya
Samu kari