Siyasar Arewa
Kungiyar Arewa Young Leaders Forum (AYLF) ta bukaci gwamnan jihar Bauchi, Bala Mohammed da ya janye kalamansa tare da neman afuwar Shugaba Tinubu.
Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya ce masu zanga-zangar yunwa sun yiwa gwamnonin Arewa allurar zaburarwa. Ya ce dole a tashi tsaye domin kawo canji.
Jam'iyyar SDP ta zargi gwamnatin jihar Kogi da magoya bayan APC ta yin taron bikin murnar samun nasara a shari'ar zaben gwamnan jihar tun gabanin kotu ta yi hukunci.
Gwamna Abdullahi Sule na jihar Nassarawa ya bayyana takaici yadda yara masu karancin shekaru suka fito zanga-zanga wadanda mafi yawansu almajirai ne.
Sanata Muhammad Sani Musa ya bukaci mataimakin shugaban kasa da sauran manyan Arewa su zauna domin samar da mafita kan matsalolin yankin bayan zanga zanga.
Kimanin 'yan siyasa 4 na Arewa ne jami'an tsaro suka fara tuhuma kan zargin daukar nauyin daga tutocin kasar Rasha a lokacin zanga-zangar yunwa da ake yi.
Jesutega Onokpasa ya ce da tuni tsohon gwamnan Kogi, Yahaya Bello da takwaransa na Kaduna, Nasir el-Rufai sun kwantar da tarzomar da ta barke a yankin Arewa.
Ministan kasafi da tsare-tsare, Abubakar Atiku Bagudu ya bayyana cewa kwata-kwata albashinsa bai kai ko miliyan daya ba inda ya ce mutane ne suke zarge-zarge.
Rundunar 'yan sandan Najeriya ta ba matasan da ke fitowa zanga-zanga shawarin su dakata tukuna, domin lokaci ya yi da ya kamata a dakata saboda rikici.
Siyasar Arewa
Samu kari