Sabon Farashin Man Fetur
Kungiyar 'yan kasuwa ta makamashin man fetur ta kasa (MEMAN) ta bayyana dalilin da ya sa aka samu karancin shigo da mai, inda ya ta ce mamakon ruwa ne ya jawo.
An shiga fargabar dawowar matsalar man fetur Najeriya bayan an gano kamfanin man fetur na kasa (NNPCL) ya fada matsalar bashi, yayin da ya gaza biyan $6bn.
An kaddamar da wasu gidajen man CNG da kamfanin NNPC ya gina a Abuja, a wani bangare na gidajen man CNG 12 da aka kaddamar a lokaci daya a Legas da Abujan.
Kamfanin NNPC ya ce ya kafa dokar ta-baci kan hako mai. Ya ce wannan wani yunkuri ne na kara yawan danyen man fetur da Najeriya ke hakowa da kuma bunkasa arzikinta.
Dillalan man fetur a Najeriya sun nuna fargabar cewa da yiwuwar ba za a samu saukin da ake tsammani a fetur ba idan matatar Ɗangote ta shigo da nata kayan kasuwa.
An wayi gari da kulle gidajen mai a birnin Ibadan na jihar Oyo inda hakan ya jefa al'umma cikin matsala. Ma'aikata sun koka kan yadda lamarin ya kawo musu cikas.
Kungiyar dillalan mai ta IPMAN a jihohin Osun da Oyo tana neman yadda za ta rage farashin litar mai zuwa N557 ganin yadda kullum man ke kara tsada.
Kamfanin man fetur na NNPC ya ƙaryata rahotannin da ke yawo a soshiyal midiya cewa ya zabtare farashin man fetur. Rahoton sabon farashin fetur "ƙanzon kurege ne."
Hukumar kula da kiyaye hakkin masu saye (FCCPC) ta shawarci gwamnatin tarayya ta buɗe iyakokin kasar nan domin shigo da kayan abinci ta halastacciyar hanya.
Sabon Farashin Man Fetur
Samu kari