Ginin Tituna
Sanata Muhammadu Danjuma Goje ya bukaci shugaba Bola Tinubu ya saka yankin Arewa maso gabas cikin ayyukan titi da gwamnatin tarayya ke kokarin farawa.
Mutanen da ke kusa da Dangwaro flyover a kusa da titin Kano-Zaria sun shiga tashin hankali bayan hadarin babbar mota ya kashe mutane akalla 25 har lahira.
Gwamnatin Najeriya na neman rancen dala miliyan 500 daga Bankin Duniya domin gina hanyoyin karkara da kuma bunkasa kasuwancin noma a fadin kasar.
Gwamnatin jihar Kano ta kaddamar da fara gina titin karkara mai nisan kilomita 7.2 daga Mil Goma zuwa 'Yankatsari, da kilo mita 7.5 a Rijiyar Gwangwan kan N2.6bn.
Mutane shida ne ake da tabbacin ceto su daga karkashin baraguzan mahakar ma’adanai a jihar Niger bayan ruftawarsa a makon nan yayin da har yanzu wasu suka makale.
Shugaba Bola Tinubu ya amince a rika kiran titin N20 da ya taso daga 'Northern Parkway' zuwa sha tale-talen Murtala Mohammed da suna: 'titin Wole Soyinka'.
Gwamnatin Gombe za ta kashe naira biliyan 20 kan gina titi mai tsawon kilomita 18.5 a ciki da wajen kwaryar jihar. Kwamishinan ayyuka na jihar ne ya sanar da haka.
Kungiyoyin ma'aikatan dake aikin gina titunan kasar nan sun fusata biyo bayan rashin jituwa tsakaninsu da gwamnati ya yi sanadiyyar korar mambobinsu 52,000.
Akalla mutane 18 ne su ka mutu a babban titin Port Harcour Enugu da ke yankin Umuahia-Enugu a safiyar yau yayin da su ke jira a shingen 'yan sanda.
Ginin Tituna
Samu kari