Jam'iyyar PDP
Kwanaki ƙadan bayan wasu daga cikin yan PDP sun koma APC a jihar Kaduna, shugabanta, Edward Masha, ya ce daman sun ci amanar jam'iyyar a zaben 2023.
Bayan gargadin gwamnatin Bola Tinubu kan sake zaben kananan hukumomi, Gwamna Ademola Adeleke ya dage cewa za a gudanar da zaben a Osun a gobe Asabar.
Bayan hukuncin kotu da kuma rigimar da aka samu kan ikon kananan hukumomi, jam’iyyar APC ta janye daga zaben a Osun da aka shirya ranar 22 ga Fabrairun 2025.
Jam'iyyar PDP ta zargi sufetan ƴan sandan Najeriya ta hannu a yunkurin APC na kashe gwamna Ademola Adeleke na jihar Osun, ta ce duk abin da ke faruwa makirci ne.
Duk da rigimar da ta barke da aka rasa rayuka a Osun kan ikon ƙananan hukumomi, shugabannin APC na yankuna 14 da kansiloli a Osun sun koma ofisoshinsu.
PDP ta fara sayar da fom ɗin takarar gwamnan Anambra, zaɓen fidda gwani zai gudana 5 ga Afrilu, yayin da za a mika sunan ɗan takara zuwa ga INEC a ranar 22 ga Mayu.
Mukaddashin shugaban PDP na kasa, Ambasa Umar Iliya Damagum ya musanta cewa akwai rashin jituwa a tsakaninsa da sabon sakataren jam'iyya na kasa da aka nada.
Rikicin siyasa a Osun ya yi sanadiyar mutuwar mutum 6. Rundunar 'yan sanda ta tura karin jami’an tsaro don kwantar da tarzoma tare da hukunta masu haddasa rikicin.
Wani babban dan adawa a Najeriya ya ce sun fara hada kan 'yan adawa domin tunkarar APC da murya daya a zaben 2027. Za a saka Atiku da Obi a shirin.
Jam'iyyar PDP
Samu kari