Jam'iyyar PDP
Sanatan Abdul Ningi mai wakiltar Bauchi ta Tsakiya a majalisar dattawan Najeriya ya koma halartar zaman majalisa biyo bayan dakatarwar da aka yi masa.
Muƙaddashin shugaban PDP na ƙasa, Ambasada Umar Damagum ya ce suna shirin jawo tsofaffin mambobin jam'iyyar domin su dawo gida ciki har da Peter Obi Obi.
Tsohon gwamnan jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal, ya bayyana cewa 'yan Najeriya sun tafka babban kuskure ta hanyar sake zaben jam'iyyar APC a 2023.
Muƙaddashin shugaban PDP na ƙasa, Umar Damagun ya bayyana cewa lokaci ya yi da babbar jam'iyyar adawa za ta koma gidanta na asali, ya roƙi mambobi su ƙata hakuri.
Jam'iyyar Peoples Democratic Party (PDP), ta sha alwashin dawowa kan madafun ikon kasar nan a shekarar 2027. PDP ta shirya kwace mulki a hannun APC.
Gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara ya soke daukar ma'aikata 10,000 da Nyesom Wike ya yi a karshen mulkinsa inda ya zargi rashin bin tsari a daukar ma'aikatan.
Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya caccaki gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa kasa gyara Najeriya cikin shekara daya kan mulki.
Tsohon dan majalisar wakilan Najeriya, Tajuddeen Yusuf ya ce abu ne mai matukar wahala Atiku Abubakar da Peter Obi su hade guri guda domin tunkarar zaben 2027.
Dan takarar shugaban kasa a jami'iyyar Labor a zaben 2023, Peter Obi ya bayyana sharuddan yin hadaka tsakaninsa da Atiku Abubakar domin kayar da Bola Tinubu a 2027.
Jam'iyyar PDP
Samu kari