Rikicin PDP
Kwamitin gudanarwa na PDP ta ƙasa ya zauna taro jiya Alhamis a birnin Abuja ƙarƙashin muƙaddashin shugaba, Umar Damagum. An amince da gangamin Rivers.
Rahotanni sun bayyana cewa jam'iyyar PDP a jihar Kogi ta dakatar da tsohon dan takarar gwamnanta na zaben 2023 a jihar, Sanata Dino Melaye kan zargin zagon kasa.
Ana shirin gudanar da zaben gwamnan jihar Edo, Gwamna Godwin Obaseki ya yi babban rashi bayan hadimansa guda hudu sun yi murabus tare da watsar da PDP.
Wani jigo a jam'iyyar PDP, Kola Ologbondiyan ya buƙaci shugaban jam'iyyar na kasa, Umar Damagum, ya yi murabus daga mukaminsa. Ya fadi dalilansa.
Rahotanni sun bayyana cewa Umar Damagun, shugaban PDP na kasa ya dage taron kwamitin gudanarwar jam'iyyar da aka shirya yi wannan mako zuwa mako na gaba.
Tsohon gwamnan jihar Rivers, Nyesom Wike ya bayyana cewa yana fita daga PDP za ta samu matsala kuma ba za ta taba dawowa dai-dai ba saboda tasirinsa.
Edwin Clark ya umarci sufeton yan sandan Najeriya ya gaggauta cafke ministan Abuja, Nyesom Wike. Wike ya ce zai kunna wutar fitina ne a jihohin PDP a Najeriya.
Kungiyar haɗin kan al'ummar shiyyar Arewa maso Gabas ta roki shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya sauke Nyesom Wike daga matsayin ministan birnin Abuja.
Gwamnonin jam'iyyar PDP sun fusata kan kalaman da ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, ya yi. Sun bukaci jami'an tsaro su zama cikin shiri.
Rikicin PDP
Samu kari