Rikicin PDP
Tsohon ministan sufurin jiragen sama, Osita Chidoka ya yi murabus daga jam'iyyar PDP mai adawa a Najeriya inda ya ce ya hakura da siyasa gaba daya.
PDP ta koka kan zargin APC na mata Katsalandan a Kano. Ƙusa a PDP, Aminu Wali ya ce su na sane da rikicin da ke damunta. Amma APC ta musanta zargin da ake mata.
Jam'iyyar PDP ta dauki matakin ladabtarwa kan daya daga cikin 'yan majalisunta na majalisar dokokin jihar Bauchi. Ta dakatar da dan majalisa mai wakiltar Kirfi.
Wasu daga cikin shugabannin PDP na gunduma da ƙananan hukumomi sun yi zanga-zangar nuna adawa da yunkurin maido da shugaban jam'iyyar ɓa Cross River.
Gwamnonin jam'iyyar PDP sun bai wa kwamitin gudanarwa watau NWC karkashin Umar Damagum wa'adin watanni uku su kira taron kwamitin zartarwa na ƙasa.
Babbar jam'iyyar adawa ta ƙasa PDP ta sake ɗage taron kwamitin zartarwa na ƙasa watau NEC wanda ta shirya yi a makon gobe ranar 28 ga watan Nuwamba, 2024.
Shugaban marasa rinjaye a majalisar dattawa, Sanata Abba Moro ya ce babu abin da ya zame wa PDP alaƙallkai kamar rigingimun cikin gida kuma komai zai wuce.
Muƙaddashin shugaban PDP na ƙasa, Umar Damagum ya musanta zargin cewa ya gana da shugabannin PDP na jihohi ne da wata manufa, ya ce daman sun saba irin wannan taron
Tsohon ɗan takarar gwamnan jihar Ogun a inuwar PDP, Segun Sowunmi ya ce shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ne ya jefa jam'iyyar a cikin halin da take ciki.
Rikicin PDP
Samu kari