Jihar Osun
20 ga Agusta ta kowace shekara na zama ranar hutu a jihohin Oyo, Lagos, Ogun da Osun don bikin Isese, amma Ondo da Ekiti ba su amince da ranar hutun ba tukuna.
Gwamna Ademola Adeleke na jihar Osun ya karyata rahotannin da ke yawo cewa ya gama shirin shiga jam'iyyar haɗaka ADC, ya ce yana nan daram a PDP.
Tsohon gwamnan Osun, Gboyega Oyetola, ya ce ba zai tsaya takarar gwamna a 2026 ba domin ba wa sabbin jiga-jigai dama yayin da ake shirin gudanar da zaɓe.
Yayin da ake jita-jitar gwamnan PDP zai koma APC, jam'iyyar ta ƙi karɓar Gwamna Ademola Adeleke saboda bai da tasiri kuma zai iya lalata sunanta.
Yan adawa sun tada rigima da ƴan Majalisar 3 daga Osun da Edo suka fice daga PDP zuwa APC mai mulki, sun nemi a kwace kujerunsu bisa tanadin kundin tsarin mulki.
Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio ya karaɓta takardun sauya sheƙar sanatoci huɗu daga PDP zuwa APC a zamansu na ranar Laraba, 23 ga watan Yuli, 2025.
Yayin da ake ta shirye-shiryen zaben 2027, Gwamna Ademola Adeleke da shugabannin PDP na jihar Osun sun goyi bayan Bola Tinubu a zaben da ke tafe.
Sanata mai wakiltar Osun ta Tsakiya a Majalisar Dattawan Najeriya. Olubiyi Fadeyi ya sanarda ficewarsa daga jam'iyyar PDP saboda rigingimun da suka baibaye ta.
Jam'iyyar PDP mai adawa a Najeriya ta gamu da koma baya a jihar Osun. Daga daga cikin sanatocinta da ke majalisar dattawa ya yi murabus daga cikinta nan take.
Jihar Osun
Samu kari