Labaran NNPC
Kungiyar SERAP ta maka kamfanin mai na kasa watau NNPCL a gaban kotu kan yadda kudi N500bn suka ɓata a 2024, ta nemi a fito a yi bayanin inda kuɗin suka makale.
Rufe matatar man Fatakwal ya haddada cece kuce tsakanin masana da masu ruwa da tsaki a harkar kan fetur, an ci gaba da kira ga gwamnati ta sayar da matatu.
Kamfanin man fetur na kasa (NNPCL), ya sanar da rufe matatar mai ta Port Harourt da ke jihar Rivers. Kamfanin ya ce ya yi hakan ne domin gudanar da gyara.
Kamfanin man Najeriya na NNPCL ya rage kudin litar man fetur a birnin tarayya Abuja. NNPCL ya rage kudin litar fetur daga N935 zuwa N910 a sassan Abuja da kewaye.
Za ku ji cewa yan Najeriya sun yi zanga-zanga a Landan, suna bukatar a mayar da Mele Kyari gida Najeriya domin fuskantar EFCC kan zargin almundahana.
Matatar man Dangote ta sanar da rage kudin litar man fetur daga N835 zuwa N825 domin saukaka wa 'yan Najeriya. Hakan na zuwa ne bayan Dangote ya gana da NNPCl
Sabon shugaban kamfanin NNPCL, Bayo Ojulari ya ce za a cigaba da aikin hako man fetur a Kolmani da ke Arewacin Najeriya da ke tsakanin jihohin Gombe da Bauchi.
Aliko Dangote ya kai ziyara NNPCL domin farfaɗo da haɗin gwiwa, bayan tangarɗar da aka samu a lokacin Mele Kyari, ana sa ran gina sabuwar alaka a tsakaninsu.
Attajirin Nahiyar Afrika, Aliko Dangote ya yaba wa Shugaba Tinubu bisa nada sabbin shugabannin kamfanin NNPCL inda ya ce sun cancanta kuma za su kawo shi ga ci gaba.
Labaran NNPC
Samu kari