Matasan Najeriya
Jami'ai da ake zargin na farin kaya ne sun cafke wani Bashir Yunusa bayan ya tallata rigar zanga-zangar da ake shiryawa a Najeriya kan yunwa da matsin rayuwa.
Kungiyar Fulani makiyaya ta bayyana cewa ba ta goyon baya kuma mambobinta ba zasu fito zanga-zanga da za a yi ƙasar nan kan yunwa da matsin rayuwa.
Dan takarar shugaban kasa a jam'iyyar Labour, Peter Obi ya zargi gwamnatin tarayya da yunkurin kama shi kan shirin zanga zangar tsadar rayuwa da ake kokarin yi.
Fitaccen lauya daga jihar Kano, Abba Hikima ya shawarci majalisar tarayya da ta tsige shugaban kasa ma damar aka ga ba zai iya magance matsalolin kasar ba.
Gwamnan jihar Kogi, Ahmed Usman Ododo ya shawarci iyaye kan hana yaransu fita zanga zanga, ya kuma ce an samu masu zanga zangar goyon bayan Bola Tinubu.
Hukumar Hisbah reshen jihar Katsina ta bayyana kamawa da lalata kwayoyi da giya da suka kai darajar miliyan sittin a karamar hukumar Funtua dake jihar.
Matashin da ya yi hudubar jefo malamai masu hana zanga-zanga daga minbari mai suna Junaidu Abdullahi ya gamu da matsala bayan jefa shi gidan yari.
Kungiyar Arewa Progressives for Good Governance ta soki tsohon Ministan matasa, Solomong Dalung kan zargin goyon bayan zanga-zanga inda ta ce rashin adalci ne.
Kungiyar Ohanaeze ta kabilar Ibo ta umurci yan kabilar su nisanci zanga zanga a dukkan sassan Najeriya saboda kaucewa fadawa rikici da suka saba yi a baya.
Matasan Najeriya
Samu kari