NLC
Maniyyatan Najeriya sun shiga cikin halin rashin tabbas yayin da kungiyoyin kwadago suka fara yajin aiki. An hana jirage jigilar maniyyatan zuwa Saudiyya.
Rahotanni sun bayyana cewa shugabannin kwadago sun isa ofishin sakataren gwamnatin tarayya da ke Abuja, ana shirin wani zama a sirrince domin daƙile yajin aiki.
Ma'aikatan gwamnati a Kano sun yi zamansu a gida domin yin biyayya ga umarnin ƙungiyoyin kwadago na ƙasa na fara yajin aiki, yan kasuwa sun fita.
Awanni bayan fara yajin aikin ma'aikata a Najeriya, Gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta kira taron kwamitin mafi ƙarancin albashi ranar Talata, 4 ga watan Yuni, 2024.
Hadimin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya caccaki kungiyoyin kwadago na NLC da TUC kan shiga yajin aikin sai baba ta gani da suka yi a fadin Najeriya.
Yayin da kungiyar kwadago ta shiga yajin aikin gama gari a wannan Litinin din, mambobinta sun tilastawa makaranta da bakuna bin umarnin yajin aiki a Kaduna.
An wayi gari babu jirgin ƙasan da ya shiga ko ya fita daga Abuja yayin da ma'aikata suka ƙauracewa wuraren ayyukansu saboda yajin aikin da ƴan kwadago suka fara.
Rahotanni sun bayyana an kwashi 'yan kallo a wani bankin Polaris da ke jihar Legas bayan da kungiyar kwadago ta NLC ta dura bankin tare da fatattakar jama'a.
Kungiyar malaman jami'o'in Najeriya (ASUU) ta umarci mambobinta da su shiga cikin yajin aikin da kungiyoyin kwadago na NLC da TUC suka fara a fadin kasar nan.
NLC
Samu kari