Hukumar Jin dadin yan sanda
'Yan bindiga da ake zargin Fulani makiyaya ne sun kashe ɗan sanda da wasu mutane uku a Benue. Fiye da 30 aka ce sun mutu a hare-haren da aka kai sassan jihar.
Mutuwar wani matashi a hannun 'yan sanda, ya fusatar da al'ummar Rano, inda suka fara zanga-zanga har ta kai ga kona ofishin ‘yan sanda na garin.
Wani dan sanda ya kashe ɗalibi da ke rubuta WAEC a Ibadan bisa kuskure, lamarin dai ya haddasa zanga-zanga da kira ga gwamna da a hukunta jami'in da ya yi harbin.
'Yan sanda sun karyata cewa jirginsu ya kai wa 'yan bindiga kaya a Kogi. Sun ce aikin tsaro ne suka gudanar tare da 'yan banga da wasu jami'an tsaro a jihar.
Rikici ya barke tsakanin Amotekun da ’yan sanda a Ondo kan wani barawo da. An je jami'an Amotekun sun yi harbe-harbe, inda 'yan sanda suka yi martani.
IGP Kayode Egbetokun ya haramta tura jami'an MOPOL zuwa tsaron manyan mutane. Ya bukaci a janye su daga ayyukan da ba su dace ba domin dawo da martabar rundunar.
Rundunar ‘yan sandan Kaduna ta ce bindigar mafarauta ce ta kashe yaro dan shekara 12 a Abakpa, ba fashewar bam ba. Ana ci gaba da bincike a kan lamarin.
An kama fitaccen mawakin Najeriya, Portable bisa zargin bata suna da tayar da husuma. Rundunar ‘yan sandan Kwara ta ce ana shirin gurfanar da shi a kotu.
Rundunar 'yan sandan Najeriya ta gudanar da ranar 'yan sanda ta farko a Najeriya. An gudanar shara, raba tallafin magani da duba marasa lafiya a jihohin Najeriya.
Hukumar Jin dadin yan sanda
Samu kari