Hukumar yan sandan NAjeriya
Bayan ta da jijiyoyin wuya kan ganin yan sanda a Kano suna taimakawa dan siyasa rabon kuɗi ga jama'a, rundunar ta tabbatar da ɗaukar matakin ladabtarwa kan jami’an.
An gano bam a gonar manomi a Dikwa, Borno, inda jami’an ’yan sanda suka kwance shi cikin nasara tare da wayar da kan jama’a game da illolin abubuwan fashewa.
Rundunar 'yan sandan Najeriya ta kama kudi Naira miliyan 6.9 da bindigogi bayan 'yan bindiga da suka karbo kudin fansa suna kokarin guduwa a jihar Nasarawa.
Rahotanni daga jihar Borno sun tabbatar da tashin wani bam da yara yan gwangwan suka dauko a bayan gari, mutum biyu sun jikkata yayin wasu 4 suka raunata.
A labarin nan, za a ji jagora a APC, Mustapha Salihu ya ce babu dalilin da zai sa ya sace akwatin zaɓe bayan jam'iyyarsa ke samun kuri'a mafi yawa a zaɓen Adamawa.
Rundunar ƴan sanda a jihar Taraba ta cafke wasu jami’an hukumar zaɓe mai zaman kanta ta kasa (INEC) tare da kwato kayayyakin zaɓe da ake zargin sun karkatar.
Wani mutum mai shekara 50 a garin Bama da ke jihar Borno, ya yanke al'aurarsa bayan tsohuwar matarsa ta ƙi komawa gidansa duk da roƙonsa da aka yi kan lamarin.
Rahotanni daga jihar Anambra sun nuna cewa an samu tashin hankali a zaben cike gurbin Sanata Andy Ubah, wanda ya koma ga Allah a watannin da suka shude.
A labarin nan, za a ji cewa jam'iyya mai mulki a Najeriya, APC ta fara kiraye-kiraye ga hukumar zaɓe INEC a kan ta soke zaɓukan cike gurbi da ke gudana a jihar Kano.
Hukumar yan sandan NAjeriya
Samu kari