Jihar Niger
Majalisar dokokin jihar Neja ta sanar da mutuwar daya daga cikin mambobinta. Mista Joseph Duza ya yi bankwana da duniya ne bayan ya yi gajeruwar jinya.
Jirgin rundunar sojojin saman Najeriya NAF ya samu nasarar murƙushe ƴan ta'adda 28 a kauyen Bassa da ke ƙaramar hukumar Shiroro a jihar Neja jiya Laraba.
Gwamnatin Neja ta yi alkawari kan fara biyan ma'aikata sabon mafi karancin albashi na N70,000 da zarar gwamnatin tarayya ta fara biyan ma'aikata sabon albashi.
Jami'an tsaron Najeriya sun samu nasarar hallaka 'yan ta'adda mutum 12 a wani musayar wuta a Neja. 'Yan ta'addan sun kawo hari ne lokacin da suka gamu da ajalinsu.
Wasu miyagun 'yan ta'adda da ake zargin 'yan kungiyar Boko Haram ne sun sake kai hari a jihar Neja. 'Yan ta'addan sun kai sabon harin ne a karamar hukumar Shiroro.
Rahotanni sun bayyana cewa wata tankar mai ta fashe bayan da ta yi karo da wata tirela a jihar Neja. Gwamnati ta ce sama da mutane 30 da shanu 50 suka mutu.
Yan bindiga sun fara saka mutane bauta a Areacin Najeriya. Yan bindiga sun fara saka mutane noma a gonakinsu. Suna kuma kwace amfanin gonar mutane.
A rahoton nan za ku ji cewa manoma a sassan Arewacin kasar nan sun shiga mugun hali bayan 'yan bindiga sun yanka masu haraji kafin su girbe amfanin gona.
An ruwaito cewa 'yan daba sun farmaki rukunin gidajen M.I Wushishi da ke Minna, babban birnin jihar Neja inda suka ba mazauna unguwar umarnin ficewa daga gidajensu.
Jihar Niger
Samu kari