Manyan Labarai A Yau
Jam'iyyar ADC mai adawa a Najeriya ta ba tsohon dan takarar shugaban kasa a zaben 2023, Peter Obi, zabi kan ya shigo a cikinta ko kuma ya kama kansa.
Fadar shugaban kasa a Benin ta yi tsokaci kan yunkurin da sojoji suka yi na kifar da gwamnatin Shugaba Patrice Talon. Ta ce sojojin ba su karbe iko a kasar ba.
Gwamnan jihar Edo, Monday Okpebholo, ya fasa kwai kan matsalar garkuwa da mutane da ake fama da ita. Ya nuna yatsa ga 'yan siyasa masu neman mulki.
Tsohon shugaban hukumar yaki da cin hanci da karbar korafe-korafen jama'a ta jihar Kano (PCACC), Muhuyi Magaji, ya bayyana dalilin da ya sa 'yan sanda suka kama shi.
Jam'iyyar YPP ta tatttara wa dan Majalisa, Hon. Uzokwe Peter kayansa ta kore shi daga jam'iyyar bayan ganin bidiyon shaidar irin cin amanar da yake mata.
Gwamnatin jihar Sokoto ta yi martani kan zargin cewa Gwamna Ahmed Aliyu ya raka takwaransa na Abia wajen ziyarar jagoran kungiyar IPOB, Nnamdi Kanu a gidan yari.
Shugaban matatar man Dangote kuma hamshakin dan kasuwa, Alhaji Aliko Dangote, ya ba da tabbacin cewa dogon layin neman man fetur ya zama tarihi a Najeriya.
Tsohon ministan shari'a, Abubakar Malami, ya musanta zargin cewa yana da hannu cikin masu daukar nauyin ta'addanci. Ya ce akwai siyasa a cikin zargin.
Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umaru Radda, ya yaba da sulhun da aka yi da 'yan bindiga. Ya ce sulhun ya jawo an samu zaman lafiya a yankunan da ke fama da matsala.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari