Manyan Labarai A Yau
Wata babbar kotun tarayya da ke a birnin Abuja ta amince da bukatar da aka nema don bincikar takarardun karatun Ministan harkokin cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo.
Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atikubl Abubakar, ya bukaci hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), da ta sauya lokacin babban zaben shekarar 2027.
Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya ba da bayanai kan yadda jami'an tsaro suka yi yunkurin cafke shi. Ya ce jami'an DSS ne ba EFCC ba.
Sanata mai wakiltar Borno ta Kudu a majalisar dattawa, Ali Ndume, ya yi hannunka mai sanda ga jam'iyyar APC. Ya ja kunnenta kan jam'iyyar adawa ta ADC.
Tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasir El Rufai ya yi ikirarin cewa ya saurari wayar Nuhu Ribadu, inda ya ji lokacin da yake ba da umarnin a kama shi a tsare.
Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya yi zarge-zarge kan jam'iyyar APC mai mulki. Ya ce tana shirin raunana ADC bayan ta ruguza PDP.
Wani jigo a APC, Cif Eze ya bayyana cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu na fargabar zaben 2027 duk da mafi yawan gwamnoni na tare da shi a jam'iyyar APC.
Gwamnatin tarayya ta sake dauko batun janye 'yan sanda daga gadin manya. Gwamnatin ta bayyana inda ta tura 'yan sandan da ke gadin manyan mutane a kasar nan.
Shugaban jam'iyyar APC na kasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya yi magana kan tazarcen Shugaba Bola Tinubu a zaben 2027. Ya ce ya kamata Arewa ta sake zabensa.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari