Manyan Labarai A Yau
Shugaban jam'iyyar APC na kasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya samu mukamin sarautar gargajiya a jihar Benue. Mai martaba Tor Tiv zai nada masa rawani.
Gwamnan jihar Neja, Mohammed Umaru Bago, ya nuna goyon bayansa ga tsarin wa'adi daya a kan mulki. Ya ce zai taimaka wajen tabbatar da jagoranci mai kyau.
An sake taso da batun mutumin da zai yi wa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu mataimaki a zaben shekarar 2027. Wasu na ganin cewa ba za a tafi da Shettima ba.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya fito ya karyata zargin kisan Kiristoci a Najeriya. Mai girma Bola Tinubu ya bayyana matsalolin da kasar nan ke fuskanta.
Hamshakin attajiirn nan, Alhaji Aliko Dangote ya bayyana cewa ya rubuta wasiyya ya barwa iyalansa kan abin da za a ware wa gidauniyarsa idan ya koma ga Allah.
Gwamna Douye Diri na jihar Bayelsa ya ayyana zaman makoki na kwanaki uku domin jimamin rasuwar mataimakinsa, Sanata Ewhrudjakpo, wanda ya rasu jiya Alhamis.
PDP ta tabbatar da mutuwar mataimakin gwamnan Bayelsa, Sanata Lawrence Ewhrudjakpo, bayan ya yanke jiki ya fadi a ofishinsa a ranar Alhamis din nan.
Wani hadimin mataimakin gwamnan jihar Bayelsa, Mr. Doubara Atasi, ya tabbatar da cewa Sanata Lawrence Ewhrudjakpo yana cikin mawuyacin hali a asibiti.
Tsohon sanatan Zamfara ta Arewa, Kabiru Marafa, ya ragargaji karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle. Ya bayyana irin taimakon da ya yi masa wajen zama gwamna.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari