Manyan Labarai A Yau
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi alhinin rasuwar mataimakin gwamnan jihar Bayelsa, Lawrence Ewhrudjakpo. Ya bayyana shi a matsayin jajirtaccen mutum.
Kotun Koli ta tabbatar da ikon shugaban kasa na ayana dokar ta-baci a jihohi, da kuma ikon dakatar da zababbun gwamnoni a shari'ar da gwamnoni PDP suka shigar.
Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya kafa sabuwar runduna ta musamman wadda za ta rika kula da tashoshin motoci da sauran wuraren da jama'a ke taruwa.
Tsohon jakadan Najeriya a kasar China, Sheikh Uthman AbdulAzeez, ya riga mu gidan gaskiya, Gwamna AbdulRahman AbdulRazak na jihar Kwara ya yi ta'aziyya.
Wani jirgin sama dauke da fasinjoji ya gamu da hatsari a filin tashi da saukar jirage na Malam Aminu Kano. An yi kokarin ceto mutanen da ke cikinsa.
Kungiyar Northern Stakeholders Consultative Initiative (NSCI) ta bukaci shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da ya ci gaba da yin aiki tare da Bello Matawalle.
Tsohon Ministan shari'a a gwamnatin marigayi Muhammadu Buhari, Abubakar Malami, ya yi sabon zargi kan hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC.
Gwamnan jihar Bayelsa, Sanata Duoye Diri, ya kadu kan mutuwar mataimakinsa. Gwamnan ya umarci a gudanar da bincike kan gawar bayan fara yada jita-jita.
Kotu a Akwa Ibom ta yankewa mutane hudu hukuncin kisa kan garkuwa da tsohon ma’aikacin ExxonMobil da yanke masa hannu bayan karbar kudin fansa N5m.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari