Manyan Labarai A Yau
Gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinde, ya sha alwashin gudanar da zaben kananan hukumomi kafin ya bar mulki a shekarar 2027. Makinde ya kuma rantsar da shugabannin 0YSIEC.
Jam'iyyar APC mai mulki a Najeriya ta shirya gudanar da babban biki domin tarbar gwamnan jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, wanda ya sauya sheka daga PDP.
Masani kan harkokin tsaro, Kabiru Adamu ya yi fashin baki kan matakin gwamnatin Bola Tinubu na sanya wasu kungiyoyi a layin 'yan ta'adda a Najeriya.
Jami'an hukumar tsaron farin kaya (DSS), sun samu nasarar yin caraf da wasu mambobin kungiyar 'yan ta'addan ISWAP. An cafke mutanen ne a cikin jihar Legas.
Gwamnan jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu ya bayyana cewa yan Najeriya za su gode wa Bola Tinubu ta hanyar sake zabensa karo na biyu a babban zaben 2027.
Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya yi rabon kayayyaki ga al'ummar Kiristoci don bukukuwan Kirsimeti. Ya bukaci a zauna lafiya da juna.
Wasu 'yan bindiga dauke da makamai sun yi awon gaba da matafiya a jihar Plateau. Tsagerun 'yan bindigan sun sace mutanen ne da ke kan hanyar zuwa Maulidi.
Wasu 'yan majalisu fuskanci barazanar kiranye daga wajen mutanen da suke wakilta. Kiranyen dai na zuwa ne sakamakon rashin gamsuwa da wakilcin da suke yi.
Amurka ta bayyana cewa ba za ta tura sojoji zuwa Najeriya ba, tana mai cewa sanya kasar cikin jerin CPC hanya ce ta diflomasiyya don karfafa gyare-gyare.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari