Manyan Labarai A Yau
Wata babbar kotun tarayya mai zamanta a birnin Abuja, ta dage shari'ar tsohon Ministan shari'a, Abubakar Malami da dansa kan zargin daukar nauyin ta'addanci.
Hamshakin attajiri kuma shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Aliko Dangote na shirin fadada harkokin kasuwancinsa. Dangote zai shiga fannin samar da lantarki.
Amurka ta bayyana jerin makaman da take amfani da su a samamen "Operation Epic Fury" da ta kaddamar a Iran. Sai dai Trump ya haramta fasahar Anthropic a yakin.
Iran ta kai wasu hare-hare kan dakarun sojojin Amurka a kasar Kuwait. Harin na Iran ya jawo an samu asarar rayukan dakarun sojojin Amurka bayan an farmake su.
Isra'ila ta rufe Al-Aqsa a Ramadan yau 3 ga Maris, 2026 saboda yaƙin Iran. An hana sallah yayin da Falasɗinawa ke zargin ƙwace ikon masallacin da ƙarfin soja.
Gwamnan jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri, ya yi magana kan zaben shugaban kasa na shekarar 2027. Ya ce ya kamata a bar Kudu ta kammala shekara takwas.
Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya yi taro da masu ruwa da tsaki na jam'iyyar PDP. Gwamnan ya tabo batun ficewa daga jam'iyyar PDP don zaben 2027.
Gwamnan jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri, ya yi magana kan komawarsa jam'iyyar APC da ke mulki a Najeriya. Gwamnan ya bayyana cewa bai shiga don ya kori wani ba.
Matatar man Dangote ta kara farashin man fetur. Karin ya shafi farashin da matatar take sayarwa ga 'yan kasuwa. Hakan na zuwa ne yayin da ake yakin Amurka da Iran.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari