Manyan Labarai A Yau
Cikakken bayani kan matakan doka 8 na tsige gwamna a Najeriya, tarihin gwamnonin da aka tsige tun 1999, da matsayar Kotun Ƙoli kan adalcin tsarin tsigewa a yau.
Ministan harkokin Abuja, Nyesom Wike ya bayyana Gwamna Siminalayi Fubara da da mara tarbiyya, wanda ya sauka daga akalar da aka ba shi gwamnatin jihar Ribas.
Hasashe ya nuna 'yan Najeriya miliyan 141 za su rayu cikin talauci a 2026; fadar shugaban ƙasa ta yi watsi da waɗannan alƙaluma, tare da fadin matakan da aka dauka.
Kwanaki kaɗan bayan sauya shekar Peter Obi zuwa ADC, Datti Baba-Ahmed ya ayyana shiga takarar shugaban ƙasar Najeriya a 2027 ƙarƙashin jam’iyyar LP,
Bayan MRS, an samu karin gidajen mai da suka hada kai da matatar Dangote kuma kungiyar IPMAN na ganin hakan zai zama alheri a farashin fetur a Najeriya.
Yara 469 ne suka mutu a Kano sakamakon rashin abinci mai gina jiki a 2025; UNICEF ta bayyana cewa kashi 51.9% na yara a jihar suna fama da matsalar tsumburewar jiki.
An gano wani babban makami mai linzami a yankin Mashegu na jihar Neja wanda ake zargin na Amurka ne; jami’an tsaro sun kwashe makamin zuwa Minna a yau don bincike.
'Yan bindiga dauke da makamai sun kai harin ta'addanci a karamar hukumar Malumfashi ta jihar Katsina. Tsagerun sun yi awon gaba da mutane masu yawa zuwa daji.
An fito da wani tsohon bidiyo na gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, yana nuna tsantsar biyayyarsa ga Rabiu Musa Kwankwaso. Ya ce ba zai masa butulci ba.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari