Manyan Labarai A Yau
Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya umarci dukkanin jami'an gwamnatinsa da masu rike da mukaman siyasa su bayyana kadarorinsu ga hukumar CCB.
Dakarun sojoji sun samu nasarar ragargazar yan ta'adda a jihar Kebbi. Dakarun sojojin sun kuma ceto mutanen da yan ta'addan suka yi garkuwa da su.
Wani mutumi ya ce ga garin ku nan bayan ya gama sheke ayarsa da wata mata a otal. Rundunar yan sandan jihar ta cafke mutum biyu da ake zargi da hannunsu a lamarin.
Shugaba Bola Tinubu ya bukaci kungiyar CAN da ta taimaka wajen yakar cin hanci da rashawa ta hanyar yin wa’azin hakuri da juriya don yan Najeriya su sauya tunaninsu.
Bayo Omoboriowo, tsohon mai daukar hoton tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya tuna yadda ya yi aiki a fadar shugaban kasa dake babban birnin Abuja.
Wasu miyagun yan bindiga sun kai sabon farmaki a jihar Ƙaduna. Miyagun yan bindigan a yayin farmakin sun yi awon gaba da wasu mutum hudu yan gida daya.
Sakataren harkokin kasar Amurka, Anthony Blinken, ya iso Najeriya inda zai gana da shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu. Blinken zai kuma gana da yan kasuwa.
Wata babbar kotu mai zamanta a jihar Rivers ta dauki mataki kan karar da aka shigar a gabanta ana kalubalantar yarjejeniyar da aka cimma tsakanin Wike da Fubara.
Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Ezenwo Wike, ya bayyana akwaiasu zuzuta matsalar rashin tsaron da ake fama da ita a birinin tarayya Abuja.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari