Manyan Labarai A Yau
Shugaban 'yan bindiga, Bello Turji, ya yi kunnen uwar shegu da rokon da wasu shugabannin Fulani suka yi masa. Ya ci gaba da kai hare-hare a Zamfara.
Jami'ar Abuja ta yi sabuwar shugaba bayan majalisar gudanrwarta ta amince da nadin Farfesa Aisha Maikudi. Nadin na ta zai yi aiki ne na tsawon shekara biyar.
Kungiyar kwadago ta kasa (NLC) ta bukaci gwamnatoci da su natsu su maida hamkali kan walwala da jindadin mutanen da suke mulki. Ta bukaci a janye kudirin haraji.
Tsohon sanata mai wakiltar Kaduna ta Tsakiya a majalisar dattawa, Shehu Sani, ya ba da lakanin hana yin cushe da ake yi a cikin kasafin kudin gwamnati.
Gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinde ya faranta ran ma'aikatan gwamnati yayin da ake bankwana da shekarar 2024. Gwamna Makinde ya cika alkawarinsa kan albashi.
An samu aukuwar hatsarin mota wanda ya ritsa da tawagar gwamnan jihar Benue, Hyacinth Alia. An samu asarar rai a lamarin wanda ya auku a ranar Lahadi.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya nuna farin cikinsa bayan matatar Warri ta dawo aiki. Shugaba Tinubu ya yabawa kamfanin NNPCL bisa wannan nasarar.
Gwamnan Jigawa, Umar Namadi ya bayyana cewa mahaifiyarsa da ɗansa Abdulwahab sun rasu ne mako guda bayan ya aurar da yarsa. ya godewa gwamnan Gombe.
Tsohon shugaban kasan Najeriya, Olusegun Obasanjo, ya bayyana masu laifi kan matsalolin da Najeriya ta tsinci kanta a cikinsu. Ya ce ba haka Allah yake so ba.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari