Manyan Labarai A Yau
Shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), Farfesa Mahmud Yakubu, ya bayyana cewa babu abin da ya samu mukaminsa na shugabancin hukumar.
Wasu 'yan ta'adda da ake zargin na kungiyar Boko Haram ne sun kai hari a waninsansanin sojoji da ke jihar Borno. 'Yan ta'addan sun kashe sojoji tare da cafke wasu.
An shiga jimami a jihar Bauchi bayan samun labarin rasuwar mukaddashin shugaban karamar hukumar Shira, Alhaji Adamu Wali. Marigayin ya rasu ne bayan jinya.
Kungiyar matasan jam'iyyar APC ta AYLCN ta bayyana cewa wasu 'yan siyasa ne ke daukar nauyin zanga-zangar da ake yi don neman EFCC ta binciki Bello Matawalle.
Gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani ya nuna matukar damuwarsa kan yadda ta'ammali da miyagun kwayoyi ke ci gaba da yaduwa tsakanin matasan Arewa.
Wasu miyagun 'yan bindiga dauke da makamai sun kai harin ta'addanci a wata makarantar sakandire da ke Zamfara. Sun hallaka wani tsohon malami tare da sace iyalansa.
Uwargidan tsohon shugaban kasan Najeriya, Dame Patience Jonathan, ta bayyana cewa ko kadan ba ta da niyyar sake komawa fadar Aso Rock Villa da ke Abuja.
Ana ci gaba da muhawara kan wakokin Mamman Shata da Dauda Rarara. Yayin da wasu ke ganin Rarara shi ne shatan zamani wasu na ganin Rarara bai kamo kafar Shata ba.
Wata kungiya karkashin jam'iyyar APC mai mulki a Najeriya ta bukaci gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, ya fito ya bayyana matsayarsa kan goyon bayan Bola Tinubu
Manyan Labarai A Yau
Samu kari