Manyan Labarai A Yau
Jami'an 'yan sanda a birnin Abuja sun harbi wasu daga cikin masu zanga-zangar nuna adawa da rushe gidajensu. An garzaya da wadanda suka jikkata zuwa asibiti.
Jam'iyyar NNPP ta fito ta yi magana bayan an yada wasu rahotanni masu cewa shugabanninta a kananan hukumomin jihar Katsina sun sauya sheka zuwa ADC.
Gwamnatin jihar Taraba ta fito ta yi magana kan rahotannin da ke cewa Gwamna Agbu Kefas na shirin sauya sheka daga jam'iyyar PDP zuwa ADC ta 'yan hadaka.
Fasto Tunde Bakare ya yi magana kan yadda aka kafa jam'iyyar APC a Najeriya. Malamin addinin ya fadi rawar da Awujale na Ijebu, Oba Sikiru Adetona ya taka.
Gwamnatin jihar Katsina ta tabbatar da cewa Gwamna Dikko Raɗda ya gami da wani ƙaramin hatsari a hanyar Daura zuwa Katsina yau Lahadi, 20 ga watan Yuli, 2025.
Jam'iyyar hadaka watau ADC ta fito ta bayyana dalilin da ya sanya Nasir El-Rufainda Peter Obi ba su fice daga jam'iyyunsu domin dawowa cikinta ba.
NDLEA ta cafke shugaban dillalan kwayoyi Okpara Chigozie tare da gano hodar iblis, methamphetamine a mota da gidansa. An kuma kama Tramadol da Rohypnol a Legas.
Gwamnatin jihar Borno ta fito ta kare kanta kan dalilin da ya sa ta kasa biyan ma'aikatan kananan hukumomi mafi karancin albaahi na N70,000 da aka amince da shi.
Tsoguwar 'yar takarar gwamnan jihar Adamawa, Sanata Aishatu Dahiru Binani ta fice daga jam'iyyar APC. Sanata Binani ta koma jam'iyyar hadaka ta ADC.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari