Manyan Labarai A Yau
Tsohon dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar SDP a zaben 2023, Adewole Adebayo, ya bayyana cewa masu komawa jam'iyyar APC na saukakawa 'yan Najeriya.
Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umaru Radda, ya bayyana cewa gwamnatinsa za ta dauki matakai kan matsalar 'yan bindiga da ta dade tana ci wa jihar tuwo a kwarya.
Kamfanin man fetur na kasa (NNPCL), ya sanar da rufe matatar mai ta Port Harourt da ke jihar Rivers. Kamfanin ya ce ya yi hakan ne domin gudanar da gyara.
Shugaban matasan jam'iyyar APGA na kasa ya koma mai ba da shawara ga Atiku Abubakar kan zaben 2027. Eze-Onyebuchi Chukwu ya bukaci Atiku ya hakura da takara.
Babban hafsan sojojin kasa , Laftanar Janar Olufemi Oluyede, ya umarci sojoji da su yi mai yiwuwa wajen kawo karshen 'yan ta'adda ba tare da nuna musu tausayi ba.
Dakarun sojojin Najeriya sun samu nasara kan 'yan ta'addan ISWAP/Boko Haram a jihar Borno. Sojojin sun hallaka 'yan ta'adda masu yawa bayan an yi dauki ba dadi.
Gwamna Abdullahi Sule na jihar Nasarawa ya bayyana cewa shi da takwarorinsa ba za su yarda a rusa hukumomin zaɓen jihohi ba, ya ce INEC kanta tana fuskantar matsala.
Hukumar gudanarwa ta Abuja watau FCTA ta bayyana cewa daga ranar Litinin, 26 ga watan Mayu, 2025, za ta karɓe kadarori 4,793 saboda ƙin biyan haraji.
Kotun kolin Najeriya ta yi watsi da karar da gwamnonin Najeriya suka ƙalubalanci gwamnatin tarayya kan yadda aka kashe kudin da aka kwato daga ɓarayin.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari