Manyan Labarai A Yau
Hukumar NCAA ta tabbatar da cewa fasinjoji 58 ba su samu damar shiga jirgin Birtish Airways da ya tashi daga Abuja zuwa Landan ba saboda matsalar kofa.
Jam'iyyar PDP ta yi martani kan sharadin da Nyesom Wike ya kafa kafin a samu zaman lafiya a cikinta. Ta ce babu wanda ya isa ya yi mata irin hakan.
Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, ya musanta cewa yana da wnai dan takara da yake goyon bayan don ya gaje shi a zaben shekarar 2027 da ake tunkara.
Hedkwatar tsaro ta kasa (DHQ) ta yi magana kan rahotannin da ke cewa tantirin dan bindiga, Bello Turji, ya mika wuya. DHQ ta ce ana ci gaba da farautarsa.
Shugaban tafiyar Obidients na kasa, Yunusa Tanko, ya bayyana cewa ya kamata tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya marawa Peter Obi baya a zaben 2027.
Tsohon dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar LP, Peter Obi, ya taso shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu kan shirinsa na kwashe kwanaki a kasashen waje.
Bayan tserewar fursunoni 16 daga gidajen yari a Keffi, an tuno yadda aka fasa gidajen yari 10 daga 2020 zuwa 2025 da adadin fursunonin da suka tsere a hare-haren.
Mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin sadarwa, Daniel Bwala, ya ba da tabbacin cewa mai girma Bola Tinubu zai samu kuri'u masu yawa a yankin Kudu maso Gabas.
Jami'an tsaro sun samu nasarar cafke wani na'ibin limamin masallacin Juma'a a jihar Sokoto kan zargin hada baki da 'yan bindiga. An samu kudade a asusunsa.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari