Manyan Labarai A Yau
Rundunar 'yan sandan jihar Plateau ta samu nasarar cafke wasu da ake zarginda hannu kan kisan da aka yi wa masu zuwa daurin aure daga Kaduna zuwa jihar.
Jami'an rundunar 'yan sandan jihar Katsina sun samu nasarar yin raga-raga da 'yan bindiga bayan sun kai wani hari. Sun ceto wasu manoma da aka sace.
Shugaban kasa Bola Tinubu ya yi Allah wadai da kisan kiyashin da aka yi wa masu zuwa daurin aure daga Kaduna zuwa jihar Plateau. Ya ce ba za a lamunci hakan ba.
A yayin da ake ta shirin tunkarar zaben 2027, hadimin Alhaji Atiku Abubakar ya musanta cewa masu son kafa hadaka sun zabi ADA a matsayin jam'iyyar su.
Wasu miyagun 'yan bindiga sun yi awon gaba da wani babban alkali a jihar Bayelsa. 'Yan bindigan sun sace alkalin ne a cikin birnin Yenagoa babban birnin jihar.
Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani, ya yi magana kan kisan da aka yi wa 'yan daurin aure a Plateau. Gwamnan ya bayyana cewa dole ne a hukunta masu laifin.
Donald Trump ya ce Amurka ta kammala kai hare-hare kan cibiyoyin nukiliya guda uku a Iran. Wannan mataki ya nuna goyon bayan Amurka kai tsaye ga Isra'ila.
Dakarun rundunar sojin Isra'ila sun yi ikirarin kakkaɓo jirage marasa matuƙa da ke ɗauke da bam waɗanda Iran ta yi nufin farmar kasar jiya da daddare.
Rahotanni na ta kara fitowa kan irin barnar da wasu gungun mutane suka yi wa masu daurin aure daga Kaduna zuwa Plateau. An kashe 'yan uwan ango a harin.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari