Manyan Labarai A Yau
Tsohon shugaban kasa, Goodluck Ebele Jonathan, ya ba da shawara kan abin da ya kamata a yi wa shugabannin da su ka gaza yin katabus a lokacin mulki.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya samu tagomashi a batun zaben shekarar 2027. Kungiyar Cagram ta yi wa Shugaba Tinubu alkawarin samun miliyoyin kuri'u.
Jam'iyyar APC mai mulki a jihar Ondo ma shirin samun karuwa ta wani babban dan siyasa. Dan takarar gwamnan PDP, Agboola Ajayi, ya shirya komawa cikinta.
Dakarun sojojin Najeriya tare da hadin gwiwar sauran jami'an tsaro, sun samu nasarar dakile wani harin 'yan bindiga a jihar Katsina. An samu nasarar ne bayan artabu.
Shugaban hukumar Alhazai ta kasa, Farfesa Abdullahi Usman, ya bayyana cewa sun yi namijin kokari wajen samar da sassauci ga Alhazai yayin aikin Hajjin 2025.
Wasu 'yan ta'adda dauke da makamai sun kai hari a wani gari da ke kan iyaka a jihar Borno. 'Yan ta'addan sun fafata da sojoji tare da kwashe makamai daga sansaninsu.
Jam'iyyar PDP mai adawa a Najeriya, ta bukaci shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya fara shirin mika mulki a shekarar 2027. Ta ce yanzu 'yan Najeriya sun waye.
Gwamna Siminalayi Fubara na jihar Ribas ya gode wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu da Ministan Abuja bisa gudummuwar da suka bayar wajen dawo da zaman lafiya.
Hukumar NCDC ta ce sakamakon gwaje-gwajen da aka yi wa wasu mutane biyu a Abuja ya nuna cewa ba sa dauke da cutar Ebola ko Marburg. Ta gargadi jihohin Najeriya.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari