Manyan Labarai A Yau
Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya naɗa Sai'du Yahya a matsayin sabon shugaban hukumar karɓar ƙorafe-ƙorafe da yaƙi da cin hanci da rashawa ta jihar Kano.
An shiga jimami a jihar Yobe bayan rasuwar daya daga cikin sarakunan da ake ji da su. Mai martaba Sarkin Gudi ya y bankwana da duniya bayan ya yi jinya.
Yaron tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, Bashir El-Rufai, ya yi bayani kan wanda ya fi damar kayar da Bola Tinubu tsakanin Peter Obi da Atiku Abubakar.
Gwamnatin jihar Katsina ta shirya kashe kudade don inganta tsaro a manyan asibitoci. Gwamnatin za ta gina katangu a wasu manyan asibitoci saboda rashin tsaro.
Gwamnatin jihar Neja ta shigar da kara a gaban Kotun Koli. Ta shigar da gwamnatin tarayya kara ne kan kin sanya ta cikin masu amfana da kaso 13%.
Rikici mai zafi ya kunno kai a jam'iyyar ADC da ƴan adawa suka yi haɗaka a cikinta, tsohon ɗan takarar gwamnan Gombe, Nafi'u Bala ya tada rigima.
'Yan bindiga sun tafka ta'asa a jihar Sokoto bayan sun farmaki manoma. Miyagun sun hallaka manoman da ke tsaka da aiki a cikin gonakinsu a wani kauye.
Kotu a Ilorin ta yanke wa Malam Abdulrahman hukuncin kisa ta hanyar rataya kan kisan Hafsoh Lawal, ta kuma wanke wasu mutum hudu da ake zargi da hannu a kisan.
Jam'iyyar hadaka watau ADC ta fito ta yi magana kan batun cewa an kafa ta ne don cika burin Atiku Abubakar na zama shugaban kasa. Ta ce sam ba haka ba ne.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari