Manyan Labarai A Yau
'Yan gudun hijira a Benue sun mamaye titi suna zanga-zanga kan halin da suke ciki duk da tallafin N1bn da uwargidar shugaban kasa ta ba su a ziyararta jihar.
Dakarun sojojin Najeriya sun samu nasarar hallaka 'yan ta'addan ISWAP a jihar Borno. Sojojin sun samu nasarar ne bayan sun yi artabu da miyagun a cikin daji.
Ruwan sama mai karfi a Maiduguri ya haifar da ambaliya, ya rushe gine-gine takwas tare da tilasta wa mutane da dama tserewa daga gidajensu a ranar Laraba.
Kamfanin man fetur na kasa (NNPCL), ya bayyana cewa ba zai sayar da matatar Port Harcourt ba. Shugaban kamfanin ya ce za a ci gaba da gyaran matatar.
Ministan harkokin yada labarai, Mohammed Idris, ya bayyana cewa mai girma Shugaba Bola Tinubu ya cika alkawuran da ya daukarwa yankin Arewacin Najeriya.
Ministan kasafi da tsare-tsaren ƙasa, Atiku Bagudu ya ce sabanin yadda ake zargi, yankin Arewa na da cikakken wakilci a gwamnatin Bola Ahmed Tinubu.
Malaman asibiti sun shiga yajin aikin gargadi na kwanaki bakwai daga yau Laraba, wanda zai shafi asibitoci 74 na tarayya da na jihohi a fadin Najeriya.
Kungiyar sanatocin Arewa ta nuna takaicinta kan kisan kiyashin da aka yi wa mutane a jihar Zamfara. Sun bukaci mai girma Bola Tinubu ya kara zage damtse kan tsaro.
Gwamnan jihar Bauchi, Bala Mohammed ya tabbatar da rasuwar shugaban hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jiha, Alhaji Ahmed Makama Hardawa a birnin Abuja.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari