Manyan Labarai A Yau
Hedkwatar tsaro ta kasa (DHQ) ta yi magana kan rahotannin da ke cewa tantirin dan bindiga, Bello Turji, ya mika wuya. DHQ ta ce ana ci gaba da farautarsa.
Shugaban tafiyar Obidients na kasa, Yunusa Tanko, ya bayyana cewa ya kamata tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya marawa Peter Obi baya a zaben 2027.
Tsohon dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar LP, Peter Obi, ya taso shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu kan shirinsa na kwashe kwanaki a kasashen waje.
Bayan tserewar fursunoni 16 daga gidajen yari a Keffi, an tuno yadda aka fasa gidajen yari 10 daga 2020 zuwa 2025 da adadin fursunonin da suka tsere a hare-haren.
Mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin sadarwa, Daniel Bwala, ya ba da tabbacin cewa mai girma Bola Tinubu zai samu kuri'u masu yawa a yankin Kudu maso Gabas.
Jami'an tsaro sun samu nasarar cafke wani na'ibin limamin masallacin Juma'a a jihar Sokoto kan zargin hada baki da 'yan bindiga. An samu kudade a asusunsa.
Gwamnatin jihar Gombe ta gabatar da kudirin kafa gundumomin ci gaba 13 don inganta mulki, magance matsalolin tsaro, da kusantar da hidima ga al’umma.
Mai alfarma sarkin Musulmi, Muhammadu Sa'ad Abubakar III, ya bukaci shugabannin Najeriya su rika sauraron koken talakawa, su gujewa musguna masu.
Gwamnan jihar Neja, Umaru Mohammed Bago, ya nada kansa mukami a kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu don tazarce a zaben 2027.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari