Manyan Labarai A Yau
NDLEA ta kama dilan kwayoyi Sunday Ibigide a Delta, ta lalata gonakin wiwi a Enugu, ta kuma kwato magungunan buguwa na biliyoyi a Rivers da sauran jihohi.
Am samu mummunar ambalihar ruwa a jihar Kebbi wadda ta lalata gidaje da gonaki. Gwamnatin Kebbi ta ba da tallafi ga mutanen da lamarin ya ritsa da au.
Jam'iyyar APGA mai mulki a jihar Anambra ta samu nasara a zaben cike gurbi na kujerar sanatan Anambra ta Kudu. Dan takarar APGA ya lallasa abokan hamayyarsa.
Jam'iyyar APC mai adawa a jihar Kano ta samu nasarar lashe zaben cike gurbi na mazabar Ghari, Tsanyawa. Ta lallasa jam'iyyar NNPP mai mulki a jihar.
Malamin addinin musulunci, Musa Yusuf Asadus Sunnah ya hadu da hatsabibin dan bindiga Bello Turji domin tattauna batun sulhu. Hakan ya sanya ya sha suka sosai.
Mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Malam Nuhu Ribadu, ya sanar da cewa jami'an tsaro sun samu nasarar cafke shugaban kungiyar 'yan ta'addan, Ansaru.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da bukatar gyara gadar Mokwa da ke jihar Neja. Shugaba Tinubu ya amince da sakin biliyoyi domin gudanar da aikin.
Jam'an tsaro sun cafke shugaban jam'iyyar PDP na jihar Ogun tare da wasu jami'an hukumar zabe ta kasa mai zaman kanta (INEC), bayan an samu kudade a wajensu.
Wasu miyagun 'yan bindida dauke da makamai sun kai harin ta'addanci a jihar Benue. 'Yan bindigan sun hallaka mutane bayan sun bude musu wuta cikin dare.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari