Manyan Labarai A Yau
Kungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN) ta bukaci gwamnatin tarayya ta kawo karshen kisan da ake yi wa Kiristoci. Ta bukaci a ba su kariyar da ta dace.
Wasu 'yan bindiga dauke da makamai sun yi awon gaba da wasu mutane a jihar Zamfara. 'Yan bindigan sun sace mutanen ne yayin wani hari karamar hukumar Bukkuyum.
Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya yi kyauta mai gwabi ga wata ma'aikaciyar lafiya 'yar asalin Anambra. Ya nuna cewa ta yi sadaukarwa a jihar.
Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya, Sanata Godswill Akpabio, ya jagoranci zaman majalisa da rantsar da sababbin sanatoci 2 daga jihohin Edo da Anambra.
Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya yi tsokaci kan rikicin Dangote da PENGASSAN. Sanusi II ya nuna cewa dole ne a kare matatar saboda muhimmancinta ga kasa.
Ambaliya ta mamaye yankunan Ogidi da Ogbaru a Anambra bayan ruwan sama mai karfi, gidaje da gonaki sun nutse, gwamnati ta dauki matakan gaggawa don taimakawa jama’a.
Gwamnan jihar Plateau, Caleb Mutfwang, ya kwararo yabo ga uwargidan shugaban kasa, Sanata Remi Tinubu. Ya ce tana nunawa jihar Plateau kauna sosai.
Rahotanni sun nuna cewa shugaban ADC na kasa, Sanata David Mark na jagorantar wani taro da sauran jagororin jam'iyyar domin ci gaba da shirye shiryen 2027.
Shugaban hukumar zaben Najeriya watau INEC, Farfesa Mahmud Yakubu ya tabbatar da sauka daga mukaminsa, tare da mika ragamar mulki ga shugabar riko.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari