Manyan Labarai A Yau
NNPCL ya ce ya gano cewa akwai kungiyoyin kasashen waje da ke da hannu a satar man Najeriya, yana mai cewa haɗin kai da hukumomin tsaro, ya sa samar da mai ya karu.
Gwamnatin Kano ta musanta zargin da ake cewa hadimin gwamna Baba Kabir Yusuf ya karkatar da Naira biliyan 6.5 daga baitulmalin jihar, ta ce sharrin siyasa ne.
Ambaliyar ruwa ta afku a Yobe, inda ta shafi gidaje 4,521 tare da raba mutane fiye da 12,000 da muhallansu. Gwamnati ta ɗauki matakan gaggawa a inda abin ya faru.
Jam'iyyar PDP ta dauki mataki kan wanda zai ci gaba da shugabantarta har zuwa lokacin da za ta zabi sababbin shugabanni na kasa. Ta daga darajar Umar Iliya Damagum.
Kamfanin sadarwa na MTN ya tabbatar da kammala gyaran turken sadarwar da aka lalata, wanda ga kawo tsaiko da katse harkokin sadarwa yankunan Kano da jihohi 2.
Tsohon mai magana da yawun marigayi Muhammadu Buhari, Garba Shehu ya yi bayani kan dalilin da ya sa tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo, ya tsani ubangidansa.
Jam'iyyar PDP ta rasa daya daga cikin jiga-jiganta a jihar Kebbi. Sanata Isa Galaudu wanda ya yi takarar gwamna ya sanar da ficewarsa daga jam'iyyar.
Tsohon mataimakin shugaban kasan Najeriya, Alhaji Atiku Abubakar, ya bayyana matsayarsa kan yin takara a zaben 2027. Atiku ya ce zai sake jaraba sa'arsa.
Jam'iyyar ADC ta nuna rashin jin dadin ta kan matakin da gwamnonin PDP suka sauka na yin taron siyasa a jihar Zamfara. Ta ce hakan rashin tausayi ne.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari